15.The Rock

  1. L̃.R. Waɗan can ãyoyin littãfi ne da abin karantãwa mai bayyanãwa
  2. Da yawa waɗanda suka kãfirta suke gũrin dã dai sun kasance Musulmi
  3. Ka bar su su ci kuma su ji dãdi, kuma gũri ya shagaltar da su, sa'an nan da sannu zã su sani
  4. Kuma ba Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da littafi sananne
  5. Wata al'umma bã ta gabãtar ajalinta, kuma bã zã su jinkirta ba
  6. Suka ce: "Yã kai wanda aka saukar da Ambato (Alƙur'ãni) a kansa! Lalle ne kai, haƙĩƙa, mahaukaci ne
  7. Dõmin me bã zã ka zo mana da malã'ĩku ba idan ka kasance daga mãsu gaskiya
  8. Bã Mu sassaukar da malã'iku fãce da gaskiya,* bã zã su kasance, a wannan lõkacin, waɗanda ake yi wa jinkĩri ba
  9. Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lale Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi
  10. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika Manzanni a cikin ƙungiyõyin farko, gabãnin ka
  11. Kuma wani Manzo bã ya zuwa gare su fãce sun kasance sunã mãsu, izgili a gare shi
  12. Kamar wancan ne Muke shigar da shi* a cikin zukãtan mãsu laifi
  13. Bã su yin ĩmãni da shi,(4( kuma haƙĩƙa, hanyar mutãnen farko ta shige)
  14. Kuma dã Mun bũɗe wata ƙõfa daga sama a kansu har suka wuni a ciki sunã tãkãwa
  15. Lalle ne dã sun ce: "Abin sani kawai, an rufe idãnuwanmu ne. Ã'a, mũ mutãne ne waɗanda aka sihirce
  16. Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun sanya waɗansu masaukai a, cikin sama, kuma Muka ƙawãta ta ga masu kallo
  17. Kuma Muka kiyãye ta daga dukan Shaiɗani wanda ake jĩfa
  18. Fãce wanda ya sãci saurãre sai wutar yũlã bayyananniya ta bĩ shi
  19. Kuma ƙasa Mun mĩkẽ ta kuma Mun jẽfa duwãtsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukan abu wanda ake aunãwa da sikẽli
  20. Kuma Muka sanyã muku, a cikinta, abũbuwan rãyuwã* da wanda ba ku zamã mãsu ciyarwa gare shi ba
  21. Kuma bãbu wani abu fãce a wurinMu, akwai taskõkĩnsa kuma ba Mu saukar da shi ba fãce kan gwargwado sananne
  22. Kuma Muka aika iskõki mãsu barbarar jũna sa'an nan Muka saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Muka shãyar da ku shi, kuma ba ku zama mãsu taskacẽwa a gare shi ba
  23. Kuma lalle ne Mu Muke rãyarwa, kuma Muke kashẽwa kuma Mũ ne magada
  24. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun san mãsu gabãta daga cikinku, kuma Mun san mãsu jinkiri
  25. Kuma lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Yake tãra su, lalle Shĩ ne Mai hikima, Masani
  26. Kuma lalle ne Mun halicci mutum daga ƙeƙasasshiyar lãka, daga baƙin yumɓu wanda ya canja
  27. Kuma Aljani Mun haliccẽ shi daga gabãni, daga wutar* iskar zafi
  28. Kuma a lõkacin da Ubangijinka ya ce wa malã'iku: "Lalle Nĩ mai halittar wani jiki ne daga ƙẽƙasasshen yumɓu wanda ya canja
  29. To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa* a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada
  30. Sai malã'iku suka yi sujada dukkansu gaba ɗaya
  31. Fãce Iblĩs, ya ƙi kasancẽwa daga mãsu yin sujadar
  32. Ya ce: "Yã Iblĩs mẽne ne a gare ka, ba ka kasance tãre da mãsu yin sujuda ba
  33. Ya ce: "Ban kasance inã yin sujada ba ga mutum wanda Ka halicce shi daga bũsasshen yumɓun lãka wadda ta canja
  34. Ya ce: "To, ka fita daga gare ta, dõmin lalle kai abin jĩfa ne
  35. Kuma lalle ne akwai la'ana a kanka har ya zuwa rãnar sakamako
  36. Ya ce: "Yã Ubangjĩna! Sai Ka yi mini jinkiri zuwa rãnar da ake tãshin su
  37. Ya ce: "To, lalle ne kanã daga waɗanda ake yi wa jinkiri
  38. Zuwa ga Yinin Lõkacin nan sanan ne
  39. Ya ce: "Yã Ubangijina! Inã rantsuwa da abin da Ka ɓatar da ni da shi, haƙĩƙa inã ƙawãta musu (rãyuwa) a cikin ƙasã kuma haƙĩƙa inã ɓatar da su gabã ɗaya
  40. Fãce bãyinKa daga gare su, waɗanda Ka tsarkake
  41. Ya ce: "Wannan tafarki ne a gare Ni, madaidaici
  42. Lalle ne bãyĩNa, bã ka da ĩkõ a kansu, fãce wanda ya bĩ ka daga ɓatattu
  43. Kuma lalle Jahannama ce haƙĩƙa, ma'akawartarsu gabã ɗaya
  44. Tanã da ƙõfõfi bakwai,* ga kõwace ƙõfa akwai wani juz'i daga gare su rababbe
  45. Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna mai idandunan ruwa
  46. Ku shigẽ ta da aminci, kunã amintattu
  47. Kuma Muka ɗẽbe abinda ke a cikin zukãtansu na daga ƙullin zũci, suka zama 'yan'uwa a kan gadãje, sunã mãsu fuskantar junã
  48. Wata wahala bã zã ta shãfe su bã a cikinta kuma ba su zama mãsu fita daga, cikin ta ba
  49. Ka bai wa bãyiNa lãbari cẽwa lalle ne Ni, Mai gãfarane, Mai jin ƙai
  50. Kuma azãbãTa ita ce Azãba mai raɗaɗi
  51. Kuma ka bã su lãbãrin bãƙin Ibrãhĩm
  52. A lõkacin da suka shiga gunsa, sai suka ce: "Sallama." Ya ce: "Lalle mũ, daga gare ku, mãsu firgita ne
  53. Suka ce: "Kada ka firgita. Lalle ne mũ, munã yi makabushãra game da wani yãro masani
  54. Ya ce: "Shin kun bã ni bushãra* ne a kan tsũfa yã shãfe ni? To, da me kuke bã ni bushara
  55. Suka ce: "Munã yi maka bushãra da gaskiya ne, sabõda haka, kada da kasance daga mãsu yanke tsammãni
  56. Ya ce: "Kuma wãne ne yake yanke tsammãni daga rahamar Ubangijin sa, fãce ɓatattu
  57. Ya ce: "To, mẽne ne babban al'amarinku? Yã kũ manzanni
  58. Suka ce: "Lalle ne mũ, an aika mu zuwa ga wasu mutãne mãsu laifi
  59. Fãce mutãnen Lũɗu, lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu tsĩrar dasu ne gabã ɗaya
  60. Fãce mãtarsa mun ƙaddara cẽwa lalle ne ita, haƙĩƙa, tanã daga mãsu halaka
  61. To, a lõkacin da mazannin suka jẽ wa mutãnen Lũɗu
  62. Ya ce: "Lalle ne ku mutãne ne waɗanda ba a sani ba
  63. Suka ce: "Ã'a, mun zo maka sabõda abin da suka kasance sunã shakka a cikinsa
  64. Kuma mun zo maka da gaskiya. Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu gaskiya ne
  65. Sai ka yi tafiya da iyãlinka, a wani yanki na dare, kuma ka bi bãyansu, kuma kada wani daga cikinku ya yi waiwaye, kuma ku bi ta inda aka aumurce ku
  66. Kuma Muka hukunta wancan al'amarin zuwa gare shi cẽwa lalle ne ƙarshen waɗancan abin yankẽwa ne a lõkacin da suke mãsu shiga Asuba
  67. Kuma mutãnen alƙaryar suka je sunã mãsu bushãra
  68. Ya ce: "Lalle ne waɗannan bãƙĩna ne, sabõda haka kada ku kunyata ni
  69. Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma kada ku sanya ni a baƙin ciki
  70. Suka ce: "Ashe ba mu hana ka daga tãlikai ba
  71. Ya ce: "Ga waɗannan, 'ya'yãna* idan kun kasance mãsu aikatãwa ne
  72. Rantsuwa da* rãyuwarka! Lalle ne sũ a cikin mãyensu sunã ta ɗĩmuwa
  73. Sa'an nan tsãwa ta kãma su, sunã mãsu shiga lõkacin hũdõwar rãnã
  74. Sa'an nan Muka sanya samanta ya kõma ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwãtsu na lãkar wuta a kansu
  75. Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi ga mãsu tsõkaci da hankali
  76. Kuma lalle ne ita, haƙĩƙa sunã a gẽfen wata hanyã tabbatacciya
  77. Lalle ne a cikin wancan akwai ãyã ga mãsu ĩmãni
  78. Kuma lalle ne ma'abũta Al'aika* sun kasance, haƙĩƙa, mãsu zãlunci
  79. Sai Muka yi azãbar rãmuwã a gare su, kuma lalle sũ biyun, haƙĩƙa, sunã a gẽfen wani tafarki mabayyani
  80. Kuma lalle ne haƙĩƙa ma'abũta Hijiri* sun ƙaryata Manzanni
  81. Kuma Kuka kai musu ãyõyinMu, sai suka kasance mãsu bijirẽwa daga gare su
  82. Kuma sun kasance sunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, alhãli sunã amintattu
  83. Sai tsãwa ta kãma su sunã mãsu shiga Asuba
  84. Sa'an nan abin da suka kasance sunã tsirfantãwa bai wadãtar ga barinsu ba
  85. Kuma ba Mu halicci sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu ba fãce da gaskiya. Kuma lalle ne Sã'a (Rãnar Alƙiyãma) haƙĩƙa mai zuwa ce. Sabõdahaka ka yi rangwame, rangwame mai kyau
  86. Lalle ne Ubangijinka, shi ne Mai yawan halitta, Masani
  87. Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bã ka bakwai waɗan da ake maimaita karatunsu* da Alƙur'ãni mai girma
  88. Kada lalle kaƙĩƙa idãnunka biyu zuwa ga abin da Muka jiyar da su dãɗi game da shi, nau'i-nau'i a gare su, kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma sassauta fikãfikanka ga mãsu ĩmãni
  89. Kuma ka ce: "Lalle nĩ nĩ ne mai gargaɗi bayyanan ne
  90. Kamar yadda Muka saukar a kan mãsu yin rantsuwa
  91. Waɗanda suka sanya Alƙur'ãni tãtsuniyõyi
  92. To, rantsuwa da Ubangijinka!* Haƙĩƙa, Munã tambayarsugabã ɗaya
  93. Daga abin da suka kasance sunã aikatãwa
  94. Sai ka tsage gaskiya game da abin da ake umurnin ka kuma ka kau da kai daga masu shirki
  95. Lalle ne Mũ Mun isar maka daga mãsu* izgili
  96. Waɗanda suke sanyãwar wani abin bautãwa na dabam tare da Allah, sa'an nan da sannu zã su sani
  97. Kuma lalle ne haƙĩƙa Munã sanin cẽwa lalle kai, ƙirjinka yanã yin ƙunci game da abin da suke faɗã (na izgili)
  98. Sabõda haka ka yi tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka kasance daga mãsu sujada
  99. Kuma ka bauta wa Ubangijinka, har mutuwa ta zo maka